1 Disamba 2021 - 14:07
An Yi Zanga zangar Kin Jinin Alakar Isra’ila Da Morocco A Rabat

A Morocco, dubban masu goyan bayan fafatukar Falasdinawa ne suka gudanar da wata zanga zanga a birnin Rabat, domin nuna adawarsu da duk wani yunkurin mahukuntan kasar na kyautata alakarta da Isra’ila.

Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {A.S} - ABNA : Zanga zangar wacce akayi a daidai zagayowar ranar tarukan ranar nuna goyon baya ga al’ummar Falastinu wacce ta gudana a jiya 29 ga wayan Nuwamba.

Yau shekara guda kenan da Morocco ta dawo da alakarta da Isra’ila, a cikin tsarin yarjejeniyar nan Abraham ta gwamnatin Amurka mai manufar daidaita alaka tsakanin Isra’ila da kasashen larabawa.

Majalisar Dinkin Duniya dai ta ayyana ranar 29 ga Nuwamba a matsayin ranar duniya ta hadin kai da nuna goyon baya ga al'ummar Falasdinu.

A ranar 29 ga watan Nuwamban shekarar 1977 Majalisar Dinkin Duniya ta amince da wannan rana, tare da yin kira ga kasashe mambobinta da su sanya wannan rana a cikin kalandarsu da kuma raya ta a kowace shekara.

342/